Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, a birnin Cape Town na Afrika ta kudu, an shirya wani taro kan jawo hankulan musulmi zuwa yawon bude a kasar, da aka yi ma take makon Halal A Afrika 2019.
James Vows daya ne daga cikin wadanda suka gabatar da jawabia wurin taron, ya babyana cewa; birnin Cape Town yana tsohon tarihin zuwa musulmi a cikinsa shekaru masu yawa da suka gabata,a akn musulmi za su iya gudanar da ayyuka a bangarori daban-daban na karfafa yawon bude na musulmi.
Daga cikin muhimman abubuwan da mahukuntan kasar Afrika ta kudu suka baiwa muhimamnci domin jawo hankulan musulmi zuwa kasar a halin yanzu dai shi ne samar da abincin halal, wanda shi ne abu na farko da musulmi suke fara nema a duk inda suke tafi.
Baya ga haka kuma akwai tsare-tsare na wuraren tarihin kasar masu jan hakula wadanda masu yawon bude kan ziyarta, wadanda za su zama daga cikin wuraren da za a rika kai musulmi domin bude ido a kasar.