Jim kadan bayan faruwar lamarin, Haramtacciyar kasar Isra'ila ta sanar da hana gudanar da sallar Juma'a a cikin masallacin mai alfarma, tare da baza jami'an soji da 'yan sanda a ciki da wajen masalalcin da kuma hanyoyin da ke zuwa masallacin, domin tabbatar da an hana gudanar da sallar juma'a acikin masallacin.
Wanann dai shi ne karon farko da haramtacciyar kasar Isra'ila ta hana gudanar da sallar Juma'a baki daya a cikin masallacin tun daga shekarar 1969, duk da cewa ta kan kayyade shekarun mutanen da za su yi sallar Juma'a a cikin wannan masallaci a wasu lokuta, inda takan kayyade mutane masu shekaru arba'in zuwa hamsin abin ya yi sama, da cewa su kadai za su sallar Jumaa a cikin masallacin mai alfarma.