Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a gobe ne za a gudaar da zaman taron makokin shahadar Imam Musa Kazem (AS) a birnin Stockholm na kasar Sweden.
Shirin zai fara ne daga karfe 19 na dare, tare da halartar masoya manzon Allah (SAW) da Ahlul bait (AS).
Hojjatol Islam Rastgo na daga cikin wadanda za su gabatar da jawabi a wurin taron.
Abin tuni a nan dai shi ne Muhaammad Mahdi Haqgoyan shi ne makarancin kur’ani na farko dan kasar Ira da ke karatu da salo 74 yana da shekaru 19, kamar yadda kuma ya dandake tafsiran Mizan, Majmaul bayan da kuma Ruhul ma’ani.