IQNA

Za A Gudanar Da Taron Karawa Juna Sani Tsakanin Na Kasa Da Kasa Na Addinan Muslunci Da Kiristanci

23:46 - December 07, 2020
Lambar Labari: 3485437
Minista mai kula harkokin addinai na kasar Masar ya ce za a gudanar da zaman taron karawa juna na malamai da masana na addinan muslunci da kiristanci.

Shafin jaridar Yaum Sabi ya bayar da rahoton cewa, ministan ma’aikatar kula da harkokin addinai na kasar Masar Muhammad Mukhtar Juma’a ya ce; za a gudanar da zaman taron karawa juna sani na malamai da masana na addinan muslunci da kiristanci nan ba da jimawa ba.

Ministan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da shugabannin mabiya addinin kirista a lardin Asyut na kasar Masar, a  wata ziyarar aiki da ya kai a lardin.

Ya ci gaba da cewa abu ne da ya zama wajibi a zauna lafiya tare da fahimtar juna tsakanin dukkanin mabiya addinai, kuma musulmi da kirista ba su da wata matsala ta rayuwa tare a tsawon tarihi, kuma shi ne da yake da muhimamnci a ci gaba da tabbatar da shi.

Bayan haka kuma ministan ya kai ziyara a masallacin Dirut, wanda yake da tsohon tarihia  kasar ta Masar, inda a halin yanzu ake batun sake gyaran masallacin.

Za A Gudanar Da Taron Karawa Juna Sani Tsakanin Na Kasa Da Kasa Na Addinan Muslunci Da Kiristanci

Haka nan kuma ya bukaci masu kula da masallacin das u dauki matakan ad suka dace domin kiyaye ka’idoji na kiwon lafiyar al’umma, musamman kasantuwar masallacin wuri ne na taruwar mutane da dama.

3939350

 

 

 

captcha