Tehran (IQNA) Cibiyar muslunci ta kasar Zambiya ta shirya bikin cikar shekarun taklifi na ‘yan mata musulmi a masallacin "Manzon Allah" da ke Lusaka, babban birnin kasar.
Taron ya samu halartar musulmi ‘yan kasashen Lebanon, india, Pakistan mazauna kasar Zambia, da kuma wasu daga cikin musulmin kasar, inda aka gabatar da jawabai na addini a wurin.