Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na IKNA daga kasar Zambiya cewa, a yammacin ranar Lahadi 26 ga watan Yuli ne aka gudanar da bukukuwan sallar Ghadir a kasar Zambiya a cibiyar musulunci ta kasar Zambiya dake birnin Lusaka fadar mulkin kasar.
Wannan bikin ya samu halartar mutane fiye da na shekarun baya. 'Yan kasar Zambiya da na Indiya da Pakistan da Lebanon da Iran da wasu kasashen Afirka da ke zaune a Zambiya sun halarci wannan bikin.
An gudanar da gasa daban-daban da shirye-shirye a cikin wannan biki, kuma an bayar da kyauta ta musamman na zagaye na biyu a Karbala ga daya daga cikin wadanda suka yi nasara a gasar, wanda dalibin kasar Zambiya ne na makarantar Islamiyya, wanda wani dan kasar Indiya ya ba da gudummawar.